Sanata Uba Sani Ne Ya Fi Dacewa Da Auren Hajiya Kaduna!

Inji Dokta Arrigasiyyu

Daga Bello Ahmadu Alkammawa

Babban Sakataren Hukumar Alhazzai ta Jihar Kaduna, Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu ya bayyana cewa tun daga lokacin da aka mayar da Najeriya a turbar dimokuradiyya zuwa yanzu, ba a taba samun wani dan siyasa da ya baiwa marada kunya ba, irin Sanata Uba Sani ta hanyar gabatar da kudurori kimanin 31 tare da aiwatar shirye shirye masu ma’ana ga rayuwar talakawa. Sakataren ya kara da cewa tun lokacin da sanatan ya dare kujerar Majalisar Dattawa domin wakiltar Gundumar Kaduna Ta Tsakiya zuwa a yau ya gabatar da ayyuka da suka dawo da martabar rayuwar talakawan Arewancin kasar a maimakon gundumar kawai.

Sakataren yana wannan bayyanin ne a yau lokacin da Gidauniyar Tunawa da Mahmud Idris a karkashin jagorancin Hajiya Hauwa’u Idris Jidda da suka kawo masa ziyara a ofishinsa, ya fada masu cewa siyasar da ake ciki a yau ta masu hankali  da tunani ce, saboda haka su yi karatun ta natsu kafin sun yanke shawarar zaben dukkanin mukaman da za a yi takara a shekarar mai zuwa, ya bayyana cewa hanya daya da za su yi amfani da ita domin sanin muhimmancin zaben dantakara shi ne sanin ayyukan da ya yiwa mutane kafin wannan lokaci, ya kara da cewa idan kuwa ta wannan hanya muhimmiya za a yi amfani to, babu ko tantama, Sanata Uba Sani zai kasance Angon Hajiya Kaduna a badi, saboda dukkanin ayyukansa da gudumuwarsa a bayyane su ke.

Shugabar Gidauniyar Hajiya Hauwa’u Idris Jidda ta bayyana cewa ganin irin muhimmancin ayyukan alherin da gidauniyar take aiwatarwa shi ne dalalin da ya sanya bayan rasuwar Alhaji Mahmud Idris ta ci gaba da kyautata rayuwar marayu da marasa galihu. Ta bayyana cewa Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu shi ne jigon samun nasarar gidauniyar, saboda kyawawan shawarorin da yake bayarwa wanda ya sanya fiye da kungiyoyi dari ke karkashin gidauniyar a yau.

A wata sabuwa, Sakataren Hukumar Alhazzan na Jihar Kaduna ya bayyana cewa, an samu canje-canje cikin tsarin gudanar da ayyukan kiwon lafiya ga alhazzai, a kowanne mataki, duk kuwa da cewa sabon fasali yana bukatar gyaran fuska saboda kalubalolin da ake cin karo da su sakamakon wannan canje-canje. Yana bayyanin ne a yau, lokacin da Ofishin Kula da Lafiya mai zaman kanshi da ake kira (Port Health Office) dake Magajin Gari cikin yankin Karamar Hukumar Kaduna Ta Arewa a Turance ya kai masa ziyara. Ya bayyana cewa Ma’aikatar Lafiya ta Kasa ta sake fasali allurar rigakafin da ake yiwa alhazzai, ya bayyana cewa jindadin su ne su ci gaba da huldar da suka saba da ofishin a can baya, to amma ba su da ikon wuce makadi da rawa saboda farantawa wani rayuwa. Ya bayyana cewa babu wata hukuma da suka mayar Saniyar ware, saboda jin dadin su ne, samun wadanda za su taimaka masu domin samun nasarar da su ke nema. Tun farko da take jawabi, Sakataren Ofishin Hajiya Aishat Isa ta bayyana damuwar ofishin ganin an mayar da su Saniyar ware a cikin ayyukan hukumar ba tare da sanin dalilin hakan ba.

An bayyana cewa baiwa nadin Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu a matsayin Babban Sakataren Hukumar Alhazzan Jihar Kaduna Gwamna Nasiru el Rufai ya sara akan gaba, saboda kasancewar wanda aka nada kwararre kuma Masanin ayyukan ci gaban Addinin Musulunci a shekaru masu yawa da suka wuce. Da yake  jawabi Kwamandan Kungiyar Lajnatul Hisbah ta Najeriya Reshen Jihar Kaduna, Malam Musa Yunusa Abu Sumayya a lokacin da ya jagorancin tawagar jami’an kungiyar domin gaisuwar ban girma ga Sakataren Hukumar Alhazzan ta Jihar Kaduna, Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu, ya bayyana cewa ba su yi mamakin wannan mukami ba, saboda sanin wanda aka yiwa shi, tunda dadewa, ya bayyana cewa hukumar za ta samu nasarori marasa misali saboda samun nagartaccen jagora.

Ya nemi sakataren ya bunkasa hukumar da ma’aikatanta, ta hanyar ba su kowacce irin dama domin su bunkasa ayyukan su, ta hanyar samun tallafi da yanayin da ya kamata domin su gudanar da ayyukan su cikin lumana da walwala. Ya nemi shi da ya baiwa ma’aikatan hukumar damar karo karatu domin su fuskanci kalubalolin ayyukan su ba tare da fargaba ba. Ya bayyanawa hukumar cewa za sub a da kowacce irin gudumuwa domin ganin hukumar na gudanar da ayyukanta cikin yanayin da take so. Ya bayyana farincikin su dangane da lambobin girma da aka baiwa sakataren a nan Najeriya da kuma Kasar Saudiyya, ya kara da cewa su kansu suna tunanin karrama shi a nan gaba.

Da yake martini, Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu ya bayyana godiyarsa ga dukkanin addu’o’in da aka yi masa, ya bayyana cewa nasarorin da hukumar ta samu a karkashinsa, kokari da jajercewar ma’aikatan hukumar ne. Babban Sakataren Hukumar Alhazzai ta Jihar Kaduna Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu ya bayyana cewa hukumar da yake jagoranci ta gwamnati ce, amma ma’aiktanta suna da ikon zaben shugabanin da su ke son su kasance a kujerun da za a yi takarar su a shekara mai zuwa, duk kuwa da cewa ido ba mudu ba ne amma yasan kima. Yana wannan tsokaci ne, lokacin da shugabanni da mambobin Farfajiyar Yakin Neman Zaben Sanata Uba Sani da Bola Tunubu suka kawo masa ziyara a ofishinsa. Ya bayyana cewa ziyartar ofisoshin gwamnati bashi ne abinda ya kamata kungiyoyin siyasa su rika yi ba, a wannan lokaci da ake kokarin ganin an samu nasarorin lashe zabe mai zuwa, ya neme su da su mayar da hankalin su ga mutane dake cikin karkara wadanda ke bukatar a wayar da kawunan su dangane dacewar zaben Jam’iyyar APC a zabe mai zuwa. Tun farko a cikin jawaban su, shugabannin farfajiyar su bayyana cewa sun shirya domin fuskantar yakin da zai kawowa Jam’iyyar APC nasara a zabe mai zuwa tun daga matakin kasa zuwa gundumomi. Saboda haka sun nemi goyan bayan mutane da ma’aikatan hukumar alhazzan Jihar Kaduna da su marawa farfajiyar goyon baya. Ko baya ga siyasa, farfajiyar tana tinkaho da kula da marayu da marasa galihu.

Hukumar Alhazzan Jihar Kaduna: Fitilar Aikin Hajji a Najeriya!

Tun lokacin da Gwamna Nasir el Rufai ya dare gadon mulkin Jihar Kaduna zuwa yanzu, Hukumar Alhazzan Jihar Kaduna ta samu nasarori wadanda suka sanya ta kasancewa sahun gaba ga takwarorinta dake Najeriya bakidaya.

Ko baya ga nagartattu ma’aikata da ake yiwa karatun ta natsu domin sanin makamar aiki, hukumar kuwa tana alfahari da kamanta gaskiya cikin lamuranta domin ganin kwaliya na biyan kudin sabulu a kowacce shekara. Wani abu da yake kara sanya hukumar sahun gaba a kullum shi ne kyakkywan yanayin da ta sami kanta a cikin a karkashin jagorancin Kwamishina Samuel Aruwan wanda shi ne ke zaman madugunta, wani dalili da ake gani ya kara sanya ta yin zarra tsakanin sauran hukumomin alhazzai dake kasar shi ne samun nagartace kuma masani harkokin addinin Musulunci a matsayin Babban Sakatarenta wato Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu. Sabon babban sakatare wanda ya hada abubuwa biyu sarauta da kuma ilimi, ganin cewa ya fito da Karamar Hukumar Igabi, gidan Sarauniya Amina, mutanen wannan karamar hukuma, manyan su da kananna ana iya cewa da ilimi da mulki suka zo duniya. Saboda haka da wannan mukami ana iya cewa gwamnan ya sara akan gaba, saboda zani ce ta iske mu je mu. Dokta Arrigasiyyu dan asalin Gundumar Rigasa ne, a wata liyafa da Muryar Matasan Rigasa suka shirya masa, mutane da dama da suka yi jawabi, sun bayyana cewa aikin ya yi daidai dashi, saboda shi masani ne a fannin abinda ya shafi ilimin Addinin Musulunci, saboda haka sun nemi shi ya kasance farin jekada ga yankin domin ganin ya samar da nasarorin da suka dace wadanda za su kara daga martabar wannan hukumar da kuma Rigasa gabadaya.

A cikin jawabinsa, Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyun ya yiwa mutane godiya kwarai da wannan karimci da aka yi masa. A cikin wata hira da manema labarai ya bayyana cewa babu yadda hukumar za ta samu nasarorin da take nema, ko baya ga aikin Hajji, tana kuma wayar da kawunan mutane musamman Musulmi birni da kauye yadda za su gudanar da addinin su, sai da taimakon kafafen yada labarai a kowanne mataki. Wannan ne dalilin da ya sanya shi kai ziyara a gidajen yada labaran dake cikin dake cikin babban birnin Jihar Kaduna, inda ya nemi su hada hannu da ofishinsa domin ganin an samu nasarorin da ake nema, ta hanyar ingatattun shirye-shirye da za su taimakawa hukumar wajen bunkasa ayyukanta birni da kauye domin ta sami nasarorin gudanar da ayyukanta cikin yanayin da ya kamata daga nan Najeriya zuwa Kasa Mai Tsarki a kowacce shekara.

A nata bangaren hukumar tana gabatar tarukkan karawa juna sani ga ma’aikatanta lokaci lokaci domin su kasance cikin shiri a kowanne lokaci, wani dalilin kuma domin su iya magance kowanne kalubale ya zo gaban su, akan hanyar su ta kaiwa ga nasara. Ana kara ilimantar da su dangane kasancewa masu gaskiya da rikon amana tare da aiki tukuru domin ganin hukumar ta samar da dukkanin nasarorin ayyukanta na ilimantar Musulmi wannan muhimmin aiki da yake daya daga cikin Shikashikan Musulunci Biyar. Hukumar tana da manya da kananna cibiyoyi a dukkanin Kanannan Hukumomin Jihar Kaduna 24 da kuma Ofisoshin Shiyya domin samun nasarorin da ake nema a kowanne mataki. Haka kuma hukumar tana babbar Cibiya a Biranen Makka da Madina, da wasu muhimman garuruwa domin ganin maniyyata daga Jihar Kaduna suna samun kyakkyawar kulawar da ta kamace su domin su gudanar da ibadar su cikin kyakkyawan yanayin da yakamata. Hukumar a karkashin Kwamishina Samuel Aruwan tana taka muhimmiyar rawa wajen ganin maniyyata da sauran wadanda keyi masu hidima daga nan Najeriya zuwa Kasar Makka suna cikin kyakkyawan yanayin tsaro, wannan ya sanya, matsalolin bacewar kudi ko kayayyaki suka kasance tarihi a cikin wadannan shekaru da wannan gwamnati ke jagoranci, an yi nasarar hada hukumar da duniya, ta hanyar samar da dandalin duniyar gizo da sauran kayayyakin da za su karawa miyar hukumar magi a cikin da wajen kasarnan.

Alkammawa ya rubuta da Unguwar Sarkin Musulmi Muhammadu Bello Kaduna, tare da rahoton Alhaji Sani Salisu Anchau, Jami’in Yada Labarai na Hukumar Alhazzan Jihar Kaduna, Numbar Salula: 07030399110 08155092812 Birnin Gwamna Kaduna.