Pilgrims Training Manuals: States to Partner with Kaduna!

By Bello Ahmadu Alkammawa

The Executive Secretary Kaduna Pilgrims Welfare Agency, Dr. Yusuf Yakubu Arrigasiyyu received the completed Comprehensive Hajj Training Manual rendered in both Hausa and English languages and as well as the Pilgrim Hajj Guide and its Hausa version called ‘Jagoran Mahajjata’ produced by the 12-Man Committee.

Speaking while receiving the report, Dr. Yusuf Yakubu Arrigasiyyu reveals that the agency will be going to reproduce copies of the work for distribution to intending pilgrims and pilgrims trainers after it is launched. He added that some State’s Pilgrim Welfare Boards have approached the agency for copies of the work the guide then in developing similar resources in their states. He thanked the committee for a good job, and he went further and added that the manuals have now been upgraded in line with global best practices and current knowledge. The agency according to him will advertise to the general public for those interested in standardized pilgrims training to apply and be screened for the Adhoc duty of training. The trainers will be trained by the committee for them to train the intending pilgrims in a proper way for the successful exercise. He said the manual will be reviewed after five years.

Dr. Arrigasiyyu said the effort and the tremendous achievements recorded are in line with Governor el Rufai’s policies toward uplifting the living standard of the pilgrimage system in the state. The agency according to him will continue to bring innovation that will not only actualize the dreams of the present administration but will keep its flag flying in taking the agency to stardom.

The agency under the sage has been rated among the best State in the 2022 Hajj Operation which was conducted successfully without many problems and received certificates of award and appreciation from both in National Hajj Commission of Nigeria and Saudi Arabia in general.

Earlier in her speech, the Chairperson of the Committee, Dr. Hadiza Ahmad Tukur of Ahmadu Bello University Zaria expressed gratitude to Allah for the opportunity given to them to be part of the history of the agency in reviewing the manuals in both Hausa and English languages that will give a successful exercise from Nigeria to Holy Land. She thanked the agency for their courage and cooperation in the completion of their work promptly.

Alkammawa writes from Sultan Bello Road Kaduna, 07030399110

Jagorancin Jihar Kaduna: ‘Yan Takarar Gwamnan Na Jam’iyyun Adawa Za Su Hade Da Sanata Uba Sani Kafin Zaben 2023! Inji Sardaunan Ikulu

Daga Bello Ahmadu Alkammawa

AISHA wannan suna yana da girma da kima da daraja tun duniyar da, da kuma a yau, suna ne mai daraja a addinin Musulunci saboda kasancewarsa ga daya daga cikin Matan Manzon Allah SAW watau Nana Aisha Allah ya kara yarda da ita amen.

Wannan suna duk ‘yar dake dashi za ka same ta da Kyawo, Natsuwa, Jarumtaka, Ilimi, Hikima, Hakuri, Juriya, Hazaka, Basira, Tausayi Wadatar Zuciya, Tsoron Allah da kuma Kishi mai girma wanda yake sanya su cin nasarar abu komai yawan kalubalen dake cikinsa. Idan haka zancen yake to bai kamata wani ya yi mamaki irin namijin kokarin Hajiya Aisha Umar ba, wadda saboda jajercewa da hazaka da kuma gwagwarmayar ta, ta kasance Kansankalin kowanne irin yakin da zai kawowa al’umma ci gaba a kowanne mataki, masu arziki da mataulata, maza da mata, yara da tsofaffi.

A yau kuma tana cikin taurarin Jam’iyyar APC a kowanne mataki, domin nasibin iya hulda da mutane da ake tunanin cikin jininta yake. Saboda haka wadanda suka san wani abu game da ita, ba su cika da wani mamaki ba, dangane da yadda ta hada wani gangamin mata tare da amfani da iliminta na hulda da mutane wajen nemowa Jam’iyyar su karin magoya baya maza da mata da suka fito da babbar Gundumar Mai Burji dake cikin yankin Karamar Hukumar Kaduna Ta Arewa wadanda suka canza sheka daga Jam’iyyar PDP zuwa APC. Kasancewar taron na farar Kaza, mata sun cika wajen gwanin ban sha’awa, ko baya ga karbar sababin magoya baya, an kuma tara miliyoyin Nairori ta hanyar wata Mujallar Siyasa da aka kaddamar a wajen bukin, bugu da kari kuma an kaddamar da sabon ofishin jam’iyyar na zamani a cikin wannan mashahuriyyar gunduma da ta kasance tsarar karamar hukumar.

Da yake jawabi a Shugaban bukin, Alhaji Ismaila Yusuf Ashafa ya bayyana farincikin tare da godiya ga Allah da ya albarkaci Jam’iyyar APC ta Najeriya da Hajiya Aisha Umar saboda a cewarsa ta hanyarta jam’iyyar tana dada samun karbuwa ga al’umma a kowanne mataki. Ya bayyana cewa zai yi kyau idan sauran matan jam’iyyar suka yi koyi da ita, domin ganin an samu gagaruma nasara a Babban Zaben 2023. Shugaban bukin wanda har illa yau shi ne Sardaunan Kasar Ikulu ya bayyana cewa akwai tabbatattun rahotannin da ke nunawa cewa wasu ‘yan takarar mukamin gwamna a Jihar Kaduna za su hade da Sanata Uba Sani kafin zaben mai zuwa, saboda su kaucewa bata rawar su da tsalle, ganin cewa jagorancin jihar na jarumi ne wanda ya amsa sunansa ta hanyar aiwatar da ayyuka da aka jima ba a gani ba.

Sardaunan Ikulu wanda jigon Jam’iyyar APC ne ga Kanannan Hukumomin Kudancin Jihar Kaduna, ya nemi ‘ya’yan jam’iyyar su kaucewa yin zaben Shinkafa da Wake domin kada su sanyawa tuwon jam’iyyar kasa a cikin kyakkyawar niyyar jagorancin jihar a badi. Ya nemi ‘yan jam’iyyar su zabi dukkanin ‘yan takarar dake karkashin innuwar APC daga sama har kasa.

Da yake jawabi a wajen bukin, babban bako kuma babban Daraktan Yakin Neman Zaben Sanata Uba Sani, Alhaji Saddik Mamman Legas, ya bayyana cewa samun ‘ya’yan yankin mazabar Mai Burji cikin jam’iyyar wawan kamu ne, saboda kasancewar mazabar a matsayin tsarar Karamar Hukumar Kaduna Ta Arewa saboda yadda take samar da rabin kudaden harajin karamar hukumar saboda kasancewarta cibiyar kasuwanci ta ji da ba da labari. Alhaji Mamman Legas wanda tsohon shugaban karamar hukumar ne, ya bayyana cewa samun magoya baya daga wannan mazabar babbar nasara ce da tabbatar da namijin kokarin Hajiya Aisha Umar.

A cikin jawabinsa Shugaban Jam’iyyar APC na Karamar Hukumar Kaduna Ta Arewa, Alhaji Suleiman Wada ya bayyana cewa  za su ci gaba da baiwa mata kowanne irin goyon baya domin su baiwa marada kunya kamar yadda suka saba. Ya bayyana cewa ta hanyar bude wannan ofishi da Hajiya Aisha Umar tayi kokari samarwa kadai ya isa masoyan jam’iyyar su gane cewa mata ne ke rike da tutar yakin neman zaben da zai kawo nasara ga jam’iyyar a Babban Zabe mai zuwa.

A cikin jawabinsa, Shugaban Kungiyar Yakin Neman Zaben Sanata Ahmad Bola Tunubu a Jihar Kaduna, Alhaji Musa  Mubama, ya bayyana cewa dukkanin wanda ya san tarihin Hajiya Aisha Umar ba zai taba mamaki da wannan gagarumin taro da ta hada ba, saboda irin kokarinta da taimakonta ga marasa galihu, wanda hakan ya sanya maigidanta ba ta dama domin ta shiga cikin shirin ginin al’umma a siyasance.

Ya bayyana cewa Dantakarar Shugaban Kasa na Jam’iyyar APC Sanata Ahmad Tunubu bashi bukatar gabatarwa domin dimbin nasarorin da ya samar a dukkanin mukaman da ya rike ko baya ga gidaunoyoyin da ya yi amfani da su wajen ginin al’ummommi a kowanne sako da lungu na kasarnan. Ya bayyana cewa lokaci ya zo da za a mayar da buki, ta hanyar zabensa domin ya kasance shugaban kasa a zabe mai zuwa. Da yake jawabi , goggage kuma daya daga cikin wadanda suka yi gwagwarmayar siyasa tun lokacin Marigayi Alhaji Shehu Shagari, Alhaji Musa Kuriga ya bayyana cewa ya kamata ‘ya’yan jam’iyyar su kawar da kunnuwan su daga sauraren mayaudara wadanda ke zancen cewa Tunubu bad an Arewa ba ne, alhali an dade ana ruwa kasa kuma na shanyewa, ya bayyana cewa sun gaji da gafara Sa amma har yanzu ba su ga kaho ba. Ya bayyana cewa Tunubu shi ne ya fi dacewa ya kasance magajin Shugaba Buhari kamar yadda Sanata Uba Sani ya fi dacewa da kasancewa magajin Gwamna Nasiru el Rufai domin ya ci gaba da aiwatar da ayyukan ci gaba domin mayar da kasar da jihar wata sabuwar Landan tare da walwala da karuwar arziki.

Da yake kaddamar da mujalla, Sardaunan Ikulu kuma Shugaban Gidan Gonar Sardauna, ya sayi kwafin mujallar guda biyar Naira Miliyan daya, an tara miliyoyin nairori tare da gabatar da taron cikin nishadantarwa da annashuwa. Sai dai ya kamata a rika sanya nagartattun jami’an tsaro a dukkanin taron siyasa domin kaucewa barazanar ‘yan jagaliya. Fitattun mata masu jini a jika da dama suka halarci buki cikin su, akwai Hajiya Zainab Tatari Ali, Hajiya Saratu Abdulazzez, da kuma Gimbiya Lubabatu Musa Ishaq da wasu da dama.

Alkammawa ya rubuta, daga Unguwar Sarkin Musulmi Bello, salula 07030399110

Sabon Gari Pilgrims Office: Stitch in A Time…

By Bello Ahmadu Alkammawa


Since the time Dr. Yusuf Yakubu Arrigasiyyu assumed duty as Executive Secretary of Kaduna State Muslims Pilgrims Agency to date, tremendous achievements was continued to be recorded which make the agency champion the cause behind its establishment. However, an investigation report carried out by this blogger indicated that there are other centers of the agency that need urgent attention one of them is Sabon Gari Local Government Pilgrims Registration Center Dogarawa.
Right now the center is completely ruined due to inadequate facilities that will add a volume of running the exercise in a conducive atmosphere that will give birth to development that will champion the cause of pilgrims of that axis. Such problems include an incomplete hall for pilgrims’ enlightenment with plastic chairs, the hall has the capacity of taking a large number of intending pilgrims at a time. Lack of office equipment, such as stationery, computers, and furniture, to add salt to existing injuries the center lacks water facilities, a standard electricity supply, and a good number of toilets for both staff and pilgrims among others.
There is a need for both the agency and the local government to join hands together in making the above-mentioned problems history of the past, for the smooth running of the exercise from Nigeria to the Holy Land. When such centers was equipped the challenges facing the agency will be minimized. The Dogarawa Center has become a home to many local governments from the northern part of the state in carrying out Hajj activities and other related issues with the good aim of carrying the agency to stardom. It was therefore timely for the center to come back to the limelight.
Alkammawa writes from Kaduna, 07030399110 belloahmadualkammawa@gmail.com

Sanata Uba Sani Ne Ya Fi Dacewa Da Auren Hajiya Kaduna!

Inji Dokta Arrigasiyyu

Daga Bello Ahmadu Alkammawa

Babban Sakataren Hukumar Alhazzai ta Jihar Kaduna, Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu ya bayyana cewa tun daga lokacin da aka mayar da Najeriya a turbar dimokuradiyya zuwa yanzu, ba a taba samun wani dan siyasa da ya baiwa marada kunya ba, irin Sanata Uba Sani ta hanyar gabatar da kudurori kimanin 31 tare da aiwatar shirye shirye masu ma’ana ga rayuwar talakawa. Sakataren ya kara da cewa tun lokacin da sanatan ya dare kujerar Majalisar Dattawa domin wakiltar Gundumar Kaduna Ta Tsakiya zuwa a yau ya gabatar da ayyuka da suka dawo da martabar rayuwar talakawan Arewancin kasar a maimakon gundumar kawai.

Sakataren yana wannan bayyanin ne a yau lokacin da Gidauniyar Tunawa da Mahmud Idris a karkashin jagorancin Hajiya Hauwa’u Idris Jidda da suka kawo masa ziyara a ofishinsa, ya fada masu cewa siyasar da ake ciki a yau ta masu hankali  da tunani ce, saboda haka su yi karatun ta natsu kafin sun yanke shawarar zaben dukkanin mukaman da za a yi takara a shekarar mai zuwa, ya bayyana cewa hanya daya da za su yi amfani da ita domin sanin muhimmancin zaben dantakara shi ne sanin ayyukan da ya yiwa mutane kafin wannan lokaci, ya kara da cewa idan kuwa ta wannan hanya muhimmiya za a yi amfani to, babu ko tantama, Sanata Uba Sani zai kasance Angon Hajiya Kaduna a badi, saboda dukkanin ayyukansa da gudumuwarsa a bayyane su ke.

Shugabar Gidauniyar Hajiya Hauwa’u Idris Jidda ta bayyana cewa ganin irin muhimmancin ayyukan alherin da gidauniyar take aiwatarwa shi ne dalalin da ya sanya bayan rasuwar Alhaji Mahmud Idris ta ci gaba da kyautata rayuwar marayu da marasa galihu. Ta bayyana cewa Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu shi ne jigon samun nasarar gidauniyar, saboda kyawawan shawarorin da yake bayarwa wanda ya sanya fiye da kungiyoyi dari ke karkashin gidauniyar a yau.

A wata sabuwa, Sakataren Hukumar Alhazzan na Jihar Kaduna ya bayyana cewa, an samu canje-canje cikin tsarin gudanar da ayyukan kiwon lafiya ga alhazzai, a kowanne mataki, duk kuwa da cewa sabon fasali yana bukatar gyaran fuska saboda kalubalolin da ake cin karo da su sakamakon wannan canje-canje. Yana bayyanin ne a yau, lokacin da Ofishin Kula da Lafiya mai zaman kanshi da ake kira (Port Health Office) dake Magajin Gari cikin yankin Karamar Hukumar Kaduna Ta Arewa a Turance ya kai masa ziyara. Ya bayyana cewa Ma’aikatar Lafiya ta Kasa ta sake fasali allurar rigakafin da ake yiwa alhazzai, ya bayyana cewa jindadin su ne su ci gaba da huldar da suka saba da ofishin a can baya, to amma ba su da ikon wuce makadi da rawa saboda farantawa wani rayuwa. Ya bayyana cewa babu wata hukuma da suka mayar Saniyar ware, saboda jin dadin su ne, samun wadanda za su taimaka masu domin samun nasarar da su ke nema. Tun farko da take jawabi, Sakataren Ofishin Hajiya Aishat Isa ta bayyana damuwar ofishin ganin an mayar da su Saniyar ware a cikin ayyukan hukumar ba tare da sanin dalilin hakan ba.

An bayyana cewa baiwa nadin Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu a matsayin Babban Sakataren Hukumar Alhazzan Jihar Kaduna Gwamna Nasiru el Rufai ya sara akan gaba, saboda kasancewar wanda aka nada kwararre kuma Masanin ayyukan ci gaban Addinin Musulunci a shekaru masu yawa da suka wuce. Da yake  jawabi Kwamandan Kungiyar Lajnatul Hisbah ta Najeriya Reshen Jihar Kaduna, Malam Musa Yunusa Abu Sumayya a lokacin da ya jagorancin tawagar jami’an kungiyar domin gaisuwar ban girma ga Sakataren Hukumar Alhazzan ta Jihar Kaduna, Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu, ya bayyana cewa ba su yi mamakin wannan mukami ba, saboda sanin wanda aka yiwa shi, tunda dadewa, ya bayyana cewa hukumar za ta samu nasarori marasa misali saboda samun nagartaccen jagora.

Ya nemi sakataren ya bunkasa hukumar da ma’aikatanta, ta hanyar ba su kowacce irin dama domin su bunkasa ayyukan su, ta hanyar samun tallafi da yanayin da ya kamata domin su gudanar da ayyukan su cikin lumana da walwala. Ya nemi shi da ya baiwa ma’aikatan hukumar damar karo karatu domin su fuskanci kalubalolin ayyukan su ba tare da fargaba ba. Ya bayyanawa hukumar cewa za sub a da kowacce irin gudumuwa domin ganin hukumar na gudanar da ayyukanta cikin yanayin da take so. Ya bayyana farincikin su dangane da lambobin girma da aka baiwa sakataren a nan Najeriya da kuma Kasar Saudiyya, ya kara da cewa su kansu suna tunanin karrama shi a nan gaba.

Da yake martini, Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu ya bayyana godiyarsa ga dukkanin addu’o’in da aka yi masa, ya bayyana cewa nasarorin da hukumar ta samu a karkashinsa, kokari da jajercewar ma’aikatan hukumar ne. Babban Sakataren Hukumar Alhazzai ta Jihar Kaduna Dokta Yusuf Yakubu Arrigasiyyu ya bayyana cewa hukumar da yake jagoranci ta gwamnati ce, amma ma’aiktanta suna da ikon zaben shugabanin da su ke son su kasance a kujerun da za a yi takarar su a shekara mai zuwa, duk kuwa da cewa ido ba mudu ba ne amma yasan kima. Yana wannan tsokaci ne, lokacin da shugabanni da mambobin Farfajiyar Yakin Neman Zaben Sanata Uba Sani da Bola Tunubu suka kawo masa ziyara a ofishinsa. Ya bayyana cewa ziyartar ofisoshin gwamnati bashi ne abinda ya kamata kungiyoyin siyasa su rika yi ba, a wannan lokaci da ake kokarin ganin an samu nasarorin lashe zabe mai zuwa, ya neme su da su mayar da hankalin su ga mutane dake cikin karkara wadanda ke bukatar a wayar da kawunan su dangane dacewar zaben Jam’iyyar APC a zabe mai zuwa. Tun farko a cikin jawaban su, shugabannin farfajiyar su bayyana cewa sun shirya domin fuskantar yakin da zai kawowa Jam’iyyar APC nasara a zabe mai zuwa tun daga matakin kasa zuwa gundumomi. Saboda haka sun nemi goyan bayan mutane da ma’aikatan hukumar alhazzan Jihar Kaduna da su marawa farfajiyar goyon baya. Ko baya ga siyasa, farfajiyar tana tinkaho da kula da marayu da marasa galihu.

Kaduna Police Commissioner Sue for Peace

Kaduna Police Commissioner Sue for Peace

By Bello Ahmadu Alkammawa

The Kaduna State Police Commissioner Mr. Yekini Ayuko has called on every organization and association in the state to give peace a chance because according to him, no nation can achieve any development without a peaceful atmosphere. He made the call when he receives the Chairman Contractors Association of Kaduna State, Engineer Ahmad Baba, and his entourage in his office recently.

Mr. Ayuko informs his guest to leave peacefully with one another, as his command will do everything possible within its capabilities to contain problems militating against the security of people’s lives and their properties. He warns the association to not involve politics in its activities for them to achieve its aims and objectives amicably. ‘My command is ready to partner with any organization that will join hands with it in making Kaduna State peaceful through adhering to the laws governing the nation’. He assured them that police will continue to maintain its status of good friendship with the people, as well as create the environment for working together to achieve a noble cause that will ginger developments in the state and the country as a whole. He said no stone will be unturned in making the state peaceful, as he told his guest that the command will not fall in arms to watch anybody bringing violence or conflict that will mess up the peaceful atmosphere enjoyed by the people of the state, the command according to him is equal to the task.

Earlier in his speech, Chairman of Kaduna State Contractors Association Engineer Ahmed Baba express his appreciation to the Kaduna State Police Commissioner Mr. Yekini Ayuko for finding time to be with them despite his tight schedules of securing the state. He lauds his giant strides since his assumption to date, which he describes as a welcome development that will take both the state and the people to a greater height. He solicited a partnership between his association and the command in every area that will give room for them to work peacefully with one another. He was accompanied by the Secretary-General

Alhaji Mustapha Kusfa, assistant secretary, Hon. Bala Yunusa an Ex Officio, Alhaji Surajo Mohammed, His Personal Assistant, Hon. Surajo, Organizing Secretary, Hajia Aisha Gwandu, Alhaji Abubakar Ahmed Baba, the Public Relations Officer Mr. Jagaba, and others.

Alkammawa writes from Sultan Bello Road Kaduna. 07030399110 belloahmadualkammawa@gmail.com

Partners in Progress

By Bello Ahmadu Alkammawa

The Women Gone Green Initiative of Nigeria which houses women who are experts in gardening and environmental-related issues will partner with the Intellectual Elite Youth Association of Nigeria, Kaduna Chapter for them to champion the cause of humanity. Speaking during a courtesy visit to the Chairperson of Intellectual Elite Youth Association of Nigeria, Kaduna Chapter Princess Lubabatu Musa Ishaq, the President of the Women Gone Green Initiative Hajia Maryam Ibrahim said the initiative is a society of women that has embraced the love for nature, on the means of producing organic vegetables and herbs in our gardens.

We thrive to encourage and support women to find solace in growing their own food which is cheaper, more-healthy and above all most satisfying. It is a passion for me as it is for all those that are part of our organization. The initiative first pilot project according her was started 2years ago in her neighbourhood of Unguwan Kanawa and Unguwan Shanu all in the heart of Kaduna city where there was a need to help access vegetables staples to our people due to the urban renewal projects that stalled market activities in Kaduna State metropolis.

We reached out to some women in our neighbourhood and asked if they will be willing to grow some vegetables and herbs in their compounds. From then on we have covered 6 major Local Governments in Kaduna State which comprises of Kaduna North, Kaduna South, Igabi, Zaria, Giwa and Kudan Local Governments respectively. Hajia Maryam inform her host that they have also reached out to some state in the northern part of the country that comprises Katsina, Jigawa, Kano, Nasarawa, Niger and Federal Capital Territory, Abuja. So far the initiative garnered over 3000 women who are direct beneficiaries of gardening projects. Their limitations according to her have to do with overstretched resources which they hope will become history through their partnership with the Kaduna State Chapter of Intellectual Elite Youth Association of Nigeria.

We are aware of your presence in all the states of the federation, and your members cut across gender age and creed. Women Gone Green Initiative is elated to partner with your association for a more presence and a sustainable development to our dear nation. We are currently exploring other avenues and sources of Green energy for domestic purposes to ease the current global energy crisis, and to further utilize the opportunities in waste management.

Responding the Kaduna State Chairperson of Intellectual Elite Youth Association of Nigeria, Princess Lubabatu Musa Ishaq, expresses her appreciation to the president of the initiative and her team for the visit. She informs them that the doors of her association were widely open for them.

The chairperson describe the visit as timely going by her association’s readiness to partner with any organization that will empowered the youth and women for them to become self-reliant in their communities. She described the Women Gone Green Initiative as avenue going to use to actualize the dream of youth and women in Kaduna State and the country as a whole. She informs them that they are going to benefit from all the skills line up by her association in taking humanity to stardom. Other members of the Women Gone Green Initiative who accompanied their president for the visit include, Abdulkareem Yunusa Bala Vice President, Barrister Murtala Dahiru, Head of Legal, Hajia Fatimah B. Gana Head of the Guardian and Hajia  Na’ima Yusuf Abdu as Secretary of the initiative respectively.

Alkammawa writes from Sultan Bello Road, belloahmadualkammawa@gmail.com 07030399110

Jihar Bauchi Ta Tsaya Cak Saboda Baiwa Sarkin Katagum Sandar Mulki!

Daga Bello Ahmadu Alkammawa

GARIN Azare watau mazaunin Karamar Hukumar Katagum dake cikin Jihar Bauchi ya cika makil babu masaka tsinke saboda yadda mutane daga kowanne sako na Najeriya da kasashen waje suka cika garin a yau Assabar 12/11/2022 domin su halarci bukin baiwa Mai Martaba Sarkin Katagum Na Sha Biyu, Alhaji Umar Faruk Na II Sandar Mulki.

Da yake jawabi a wajen bukin, Kauran Bauchi, Alhaji Bala Mohammed ya gargadi sarakuna da su kaucewa shiga harkokin siyasa. Ya kara da cewa sarakunan jihar ne za a kama da laifi a duk inda aka samu rashin zaman lafiya. Kauran Na Bauchi wanda har illa yau shi ne Gwamnan Jihar Bauchi ya nemi sarakuna su wayar da kawunan talakawan su domin su rika taimakawa jami’an tsaro da kyakkyawan bayyanan da za su taimakawa domin mayar da matsalolin tsaro dake damun jihar tarihi.

Ya bayyana cewa neman sarakuna su wayar da kawunan talakawan su wajen goyon bayan gwamnatin jihar bashi da wata manufar sanya mutane su kaucewa ra’a’yoyin su dangane da siyasar da su ke so. ‘’Sarakunan Gargajiya ya kamata su kawar da kawunan su daga siyasa, a maimakon haka su ci gaba da rike girman sun a iyayen al’umma, ta hanyar kiyayewa da tsarin da ya samar da su a matsayin shugabannin al’ummomin dake karkashin su.’’ Inji shi. Gwamnan ya bayyana cewa idan sarakuna suka sanya kawunan su cikin harkokin siyasa a maimakon su rike girman su, to kuwa za su hadu da kaskanci tsakanin su da talakawan su wanda hakan zai zubar da kimar su da mutuncin su ga talakawan su. Ya bayyana cewa ya sami rahotannin da suka wasu daga cikin sarakunan jihar cikin badakalar gandun daji da kuma burtula a tsakanin talakawan su. Gwamna Bala Mohammed ya bayyana cewa dukkanin wani sarki ko ma’aikacin hukuma da aka samu yana da hannu cikin wannan badakalar za a hukunta shi.

Da yake jawabi, Mai Martaba Sarkin Katagum, Alhaji Umar Faruk Na II ya nuna jin dadinsa ga Gwamna Jihar Bauchi Alhaji Bala Mohammed saboda irin karimcin da ya nuna masa, ya yabawa gwamnan akan ayyukan raya kasa da ya aiwatar tun lokacin da ya zama gwamnan Jihar Bauchi, wadanda suka kara fitowa da jihar ta hanyar yiwa ‘yan uwanta fintikau a wannan fanin.

Sarkin ya bayyana an nada shi a wannan sarauta ne a cikin watan Disambar shekarar 2017 bayan rasuwar mahaifinsa, Marigayi Alhaji Muhammad Kabir Umar wanda ya shafe shekaru Talatin da Biyu yana rike da sarautar, Allah ya yi masa sakayya da Jannah Firdausi tare da sauran Musulmi, Ameen. Ya yabawa tsohon gwamnan jihar Mohammed Abubakar saboda tabbatar da zaben masu zaben sarki na Masarautar Katagum. A cikin jawabinsa na godiya, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Saad Abubakar III, wanda Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya godewa sarakuna da sauran manyan baki dake Najeriya da sauran kasashen waje da suka halarci bukin.

 Bukin ba da sandar ya zo ne bayan shekaru biyar da nadin nashi a matsayin sarki. Mutane da dama suka halarci wannan kasaitacen buki, sun kuwa hada da dukkanin jikokin almajiran Shehu Usmanu Dan Fodiyo 12 wadanda sarakuna ne Daular Usmaniyya ta yanzu a karkashin jagorancin Sarkin Musulmi Muhammad Saad Abubakar III, da Dantakarar Shugaban Kasa a innuwar Jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar Wazirin Adamawa da Gwamnan Jihar Sakkwato, Alhaji Aminu Tambuwal, Mutawallen Sakkwato, da tsofaffin gwamnonin Jihar Bauchi, Alhaji Adamu Mu’azu da Alhaji Isa Yuguda da Alhaji Raji Rasaki, da Ministoci da wasu kusoshin gwamnatin tarayya da jihohi.

Bukin ya kayatar kwarai ta hanyar kasaitaccen bukin Daba da aka gudanar, inda sarakuna da masu rike da sarautun gargajiya da dama suka hau dawakai masu dauke da kwaliya tamkar za a tafi jihadi. Mata musamman wadanda jinin sarauta ke gudana a jikin su, ba a bar su a baya ba, rahotanni sun nuna cewa Sarauniya Rabi’atu Umar Sa’idu tana cikin wadanda suka karawa bukin ba da sandar armashi, ta hanyar tufafin alfarma da ta sanya, tare da wasu sarakai mata, a nesa sai ka dauka Lu’u lu’u ne tsakanin taurari. A sakonta na fatan alheri ta yiwa bakin da suka halarci bukin musamman mata fatan alheri, tare da fatan kowa ya koma gidansa lafiya.

Alkammawa ya rubutu daga Unguwar Sarkin Musulmi Muhammadu Bello dake Birnin Gwamna, Kaduna, Najeriya. Salula 07030399110 imel: belloahmadualkammawa@gmail.com

Zaben 2023: Dujiman Zazzau Ne Zai Ci Gaba da Wakiltar Mu!

Inji Malam Junaidu Ibrahim Layin Shaba

Zaben da zai fi daukar hankalin ‘yan Najeriya shi ne wanda za a yi tsakanin Alhaji Samaila Suleiman Dujiman Zazzau na Jam’iyyar PDP da Malam Bello el Rufai na Jam’iyyar APC domin kasancewa wakilin mazabar Karamar Hukumar Kaduna Ta Arewa a Zauren Majalisar Wakilai ta Najeriya a babban zaben 2023 dake zuwa cikin watanni biyar masu zuwa.

Wani matashi mai sana’ar sayar da fetur, dake cikin gundumar Shaba dake cikin Karamar Hukumar Kaduna Ta Arewa, Malam Junaidu Ibrahim ya bayyanawa Dandalin Labarai na WordPress cewa Malam Samaila Suleiman ne zai ci gaba da kasancewa wakilin karamar hukumar a majalisar wakilai ta kasa saboda irin nagartaccen wakilicinsa tun lokacin da aka zabe shi a matsayin zuwa yanzu. Ya bayyana cewa Dujiman na Zazzau ya daga tuta ta hanyar samar da ayyuka bunkasar rayuwar mutane domin su kasance masu dogara ga kawunan su, domin kaucewa kowacce barazanar rayuwa, ganin aikin gwamnati ya zama sai ‘ya’yan masu hannu da shuni.

Malam Junaidu ya bayyana cewa saboda nagartar Dujiman Zazzau yake tare dashi tun lokacin da yake cikin Jam’iyyar CPC zuwa yanzu da yake PDP, ya bayyana cewa za su ci gaba da kasancewa tare dashi har sai ya daina siyasa. Ya bayyana cewa ayyukan da Dujiman ya aiwatar a bayyane su ke kuma an gabatar su a dukkanin gundumomin 12 da suka yi Karamar Hukumar Kaduna Ta Arewa, sun hada da asibitoci da makarantu da masallatai na Jumma’a da kuma na Hamsar Sallawati, ya kuma samar da famfunan tuka-tuka bilahadadin tare da bayar da tallafin kudi ga matasa maza da mata da kuma rarraba kayayyakin sana’o’in hannu na zamani ga matasa maza da mata domin su sami dogaro mai amfani.

Malam Junaidu ya kara da cewa ko baya ga ginin makarantu, ‘ya’yan talakawa da dama suka sami tallafin kudi domin gudanar da karatun su cikin yanayin da ya kamata tun daga matakin Sakandare zuwa Jami’o’in dake cikin kasarnan. Wasu kuma yanzu haka suna kasashen waje, matashin ya bayyana cewa an bunkasar rayuwar matasan da ba su yi karatu mai zurfi ba, ta hanyar koyar da su sana’o’in hannu iri daban daban domin su samu saukin rayuwa cikin fatara da talauci da Jam’iyyar APC ta jefa kasar ciki. Malam Junaidu ya kara da cewa an samar da tituna a wurare da dama a cikin karamar hukumar wadanda suka taimakawa masu ababen hawa wajen samun saukin sufuri cikin yanayin da ya kamata. Ya bayyana cewa daga cikin ‘yan takarar kujerar Alhaji Samaila Suleiman kawai ke da abun nunawa mutane a bayyane su kuma gamsu da takararsa, ya bayyana cewa wasu daga cikin masu takarar kujerar sai a wannan lokaci aka soma jin sunayen su, kuma ba wani abun da suka tsinanawa talakawa sai sharholiya.

Alkammawa ya rubuta daga Unguwar Sarkin Musulmi Muhammadu Bello dake Birnin Gwamna, Salula 07030399110 Kaduna, Najeriya.

Mista LA: Dutsen Tsakar Ruwa

kafa
Mai karatu a yau zanyi tsokaci ne akan wani bawan Allah da ya yi suna saboda tausayinsa da kyautatawarsa ga mutane musamman marasa galihu, wato Alhaji Lawal Adamu Usman wanda aka fi sani da Mista LA. A kowanne mataki ka sanya sunansa za ka ga cewa ya dace, ya dade da kasancewa a zukatan dubun dubatan mutane saboda Kyautarsa da tausayinsa wanda yake yi ba tare da kulawa da matsayin mutane ba, shi dai gurinsa mutane su kasance cikin walwala.
Daya daga cikin alheransa da zaiyi wuyar mantawa shi ne wanda ya aiwatar lokacin da Gwamnatin Jihar Kaduna a karkashin jagorancin Malam Nasiru el Rufai ta sanyawa talakawa dokar zaman gida da sunan annobar Korona. Shi ba gwamnati ba, hasalima Jam’iyyar da yake ciki watau PDP ba itace ke rike da madafun iko ba, da rana tsaka ya fito da tirelolin dauke da kayayyakin masarufi yana rarrabawa talakawa.
Ko bayan wannan lamarin jinkai da ya girgiza masu fada aji da wadanda ke rike da madafun iko a jihar, Mista LA bai tsaya nan ba, kwaram sai ya fito da shirin biyawa ‘ya’yan talakawa kudin karantu a manyan makarantun gaba da sakandare na jihar da suka yiwa talakawa kamshin dan goma, saboda tsadar kudi da aka sanya da manufar ruguza karatun ‘ya’yan talakawa. Ya kuma lura cewa mutane ba su da tsaftattacen ruwansha ba tare da bata lokaci ya shiga aikin kafa famfunan tuka-tuka saboda mayar da matsalar tarihi.
Wadannan da wasu dalilai ne suka sanya mutanen Kanannan Hukumomin Gundumar Kaduna Ta Tsakiya nemansa domin ya kasance Sanatan su Majalisar Dattawan Najeriya bayan an kai ruwa rana, ya karba. Ya kuma ci gaba da kyautatawa marasa galihu birni da kauye, babu abinda ya tsaya, taimakon ya hada da bayar da motoci, babura da kayayyakin sana’o’in hannu ga matasa da mata domin su dogara ga kansu domin kaucewa kowacce irin barazana ta rayuwa.
Watannin baya aka yi zaben fitar da gwani na jamm’iyyun siyasun Najeriya, ya kuma lashen zaben amma sai wasu da ba su da ilmin tafiyar da mutane suka kai kara Kuliya da zargin cewa akwai rashin gaskiya cikinsa, shekaranjiya kuliyar ta yanke hukuncin a sake zaben cikin kwana goma sha shida.
Shi wanda yakai karar tare da wadanda ke rike masa kan Maciji yana wasa da bindi, suna da yakinin Alhaji Lawal Adamu Usman da yardar Allah shi ne zai kasance zakara idan anyi zaben sau dubu domin jinkansa da tausayinsa da kuma irin huldarsa da mutane, wani abu kuma da yake tinkaho dashi shi ne ilimin zamani da na Islama, ko baya ga iya hulda da jama’a, kuma tuntuni ya gane matsalolin da ke ciwa gundumar tuwo a kwarya fiye da dukkanin wadanda ke takarar kujerar domin yafi sanin Kanannan Hukumomin gundumar fiye da hakoransa.
Alkammawa ya rubuta daga Unguwar Sarkin Musulmi Muhammadu Bello, Kaduna 07030399110 imel:belloahmadualkammawa@gmail.com